Sojojin Syria Sun Dawo Da Tsaro A Wasu Yankuna Da Ke Arewacin Aleppo Bayan Korar 'Yan Ta'adda

Sojojin gwamnatin Syria sun kwace iko da wasu yankuna masu matukar muhimmanci a arewacin birnin Aleppo da ‘yan bindiga ke iko da su, yayin da ake ci gaba da gwabzawa tsakanin bangarorin biyu a yankunan da ke gefen filin safka da tashin jiragen sama na birnin.

 

Kamfanin dillancin labaran SANA ya nakalto daga rundunar sojin kasar ta Syria cewa, a jiya dakarun gwamnatin sun fatattaki daruruwan ‘yan ta’adda da ke samun goyon bayan kasashen Amurka da Saudiyya daga yankuna da dama da ke arewacin Aleppo, tare da kashi wani adadi mai yawa daga cikinsu, wasunsu kuma sun tsre zuwa cikin kasar Turkiya.

A bangare guda kuma wasu rahotanni sun bayyana cewa, ‘yan ta’adda na Syria sun harba makaman roka a jiya a cikin birnin Aleppo, inda suka kashe fararen hula 9 da suka hada da kananan yara ‘yan makaranta, yayin da wani adadi mai yawa na faraen hula suka samu raunuka.

 

Ƙara sabon ra'ayi