Somaliya : Mutane 21 Suka Mutu A Harin Al'Shabab

Yan sandan kasar Somaliya sun bayyana cewa, wata fashewar boma-bomai da ake zaton na kunar bakin wake ne a yankin Baidoa dake kudancin kasar Somaliya, ta haddasa mutuwar mutane a kalla 21 tare da raunata wasu mutanen a harin da kungiyar Al'shab ta dauki alhakin kai wa a jiyya lahadi

 

 

 

'Yan sandan yankin Baidoa sun bayyana cewa, an samu fashewar bom da aka dasa cikin wata mota a wani otel dake yankin Baidoa, kana wani dan kunar bakin wake ya tada wani bom din dake jikinsa a wani otel na daban dake yankin.

Wadannan hare-haren biyu sun yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 21, yawancinsu su ne fararen hula.

Ƙara sabon ra'ayi